Hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC ta ce, a za a sake zabukan Gwamnoni a wasu mazabun jihohin da suka hada da: Kano, Bauchi, Benue, Filato, Sakkwato da Adamawa, sakamakon rashin kammala zaben da aka yi ranar 9 ga Maris 2019.
Za a dai sake zabukan ne a ranar 23 ga Maris 2019, kamar yadda shugaban kwamitin sadarwa na INEC Festus Okoye ya sanar a Abuja.
An sanar da sakamakon gwamnoni 22 cikin 29.