✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za mu yi kokarin ganin an inganta sufurin jiragen kasa

Kwamitin  kula da  harkokin  jiragen kasa da  gwamnatin  tarayya  ta nada domin inganta sufurin jirgin kasa, karkashin shugabancin Alhaji Abubakar Kawu Baraje, ya kai  ziyarar …

Kwamitin  kula da  harkokin  jiragen kasa da  gwamnatin  tarayya  ta nada domin inganta sufurin jirgin kasa, karkashin shugabancin Alhaji Abubakar Kawu Baraje, ya kai  ziyarar  gani  da  ido a tashar jirgin kasa  da ke Ikko, inda ya ce  zai nemi gwamnatin  ta kara kudi a bangaren  sufurin.
Sa’ilin da yake zagayawa, shugaban kwamitin ya ce kodayake gwamnati na hasarar kudi  a wannan wurin, amma nan ba da  jimawa  ba duk zai  zame tarihi saboda tattaunawar  da  kwamitin zai yi  da  ministan  sufuri  da shugabannin hukumar da kuma shugaban kasa don inganta harkokin jirgin kasan.
Ya ce  mayar  da  zirga-zirgar jiragen  kasa  a Najeriya,  zai  talmaka wa talaka, saboda saukinsa da  kuma raguwar hatsari.
Dangane da tsoffin kayayyaki, Alhaji Baraje  ya ce hukumar za ta  jingine su  ta  rungumi na zamani, duk dayake suna da sauran amfani.
Daga cikin injiniyoyin da ya  zagaya da kwamitin, Injiniya  Zayyana Kabir ya yi nunin komai tsufan jirgi ana iya gyara shi  muddin dai za a samu wadatattu kayan aiki, daya daga  cikin manya-manyan matsalolin da ke addabarsu, amma muddin za su samu, ba wani  taragon da zai  gagari  gyarawa a dakin gyare-gyare da ke  Ikko da Enugu da Zaria da Minna.
Yanzu  dai  jirgin kasa ya fara  aiki  daga  Legas  zuwa  Kano  sau biyu a sati.