Jam’iyyar APC ta lashe kujerun shugabannin Kananan Hukumomi 22 cikin 25 na jihar Neja, wanda aka yi ranar Asabar. Yayin da Jam’iyyar adawa ta PDP ta lashe Karamar Hukumar Gbako, kadai.
A cikin Kananan Hukumomin da APC ta lashe sun hada da: Bida, Agaie, Katcha, Lapai, Lavun, Kontagora, Rafi, Magama, Shiroro da Munya.
Sauran su ne: Suleja, Borgu, Gurara, Mariga, Mokwa, Paikoro, Wushishi, Chanchaga, Agwara, Edati, Rijau da kuma Bosso.
Shugaban Hukumar zabe na jihar (NSIEC) Alhaji Aminu Baba, ya ce a yanzu haka ana jiran sakamakon zaben Kananan Hukumomin Mashegu da Tafa.