✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zaben Kogi: An gano ma’aikatan zabe 30 da suka bace

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa (INEC) ta ce, an gano ma’aikatan Hukumar 30 da aka sanar da bacewar su, a wasu rumfunan zabe…

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa (INEC) ta ce, an gano ma’aikatan Hukumar 30 da aka sanar da bacewar su, a wasu rumfunan zabe na zaben Gwamnan jihar Kogi da aka yi jiya Asabar.

Rotimi Lawrence Oyekanmi, Sakataren watsa labarai na Shugaban INEC Farfesa Mahmood Yakubu.

Rotimi Lawrence, ya ce a yanzu ma’aikatan suna cikin koshin lafiya ba tare da wani rauni ba, kuma sun isa gidajensu.