✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An Kama ’Yan Fashin Da Suka Kashe ’Yar NYSC A Binuwai

Sun kashe Irene a lokacin da suke kokarin kwace kwanfiyutarta

’Yan sanda sun kama ’yan fashin da ake zargi da harbe wata mai yi wa kasa hidima har lahira a garin Makurdi na Jihar Binuwai. 

’Yan fashin sun kashe Irene Chioma Emmanuel, wadda ke aikin hidimar ƙasa ne a lokacin da suke kokarin kwace kwanfiyutarta, a kan titin Naka-Makurdi da ke Makurdi.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Emmanuel Adesina, ya shaida wa ’yan jarida a hedikwatar rundunar cewa ’yan fashin sun amsa cewa su ne suka kashe Irene kuma su ne suka addabi yankin da yin fashi da makami.

Adesina ya ce bayan samu rahoton lamarin, a ranar Talata 6 ga watan Fabrairun 2024, rundunar ta kai samame maɓoyar ’yan ta’addan da ke yankin Adeke, inda ta kamo wadanda ake zargin.

Ya kara da cewa a ranar Asabar 24 ga wata da dare sun cafke wasu mutane biyu a anguwar Adoka, a wani sammen haɗin guiwa da ’yan sa-kai a wani wuri da ’yan fashin ke yi wa mutane kwanton bauna.

Kwamishinan ya bayyana cewa sun kwace bindigogi da kuma katinan cirar kuɗi da dama a hannun ’yan fashin.

Ya ce ana ci gaba da bincike kan lamarin domin gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.