Kasar China ta yi gargadi mai tsauri ga masu neman canji wadanda suka janyo harkoki a Hong Kong suka tsaya cik, bayan sama da wata biyu da suka yi suna gudanar da zanga-zanga mai zafi.
Yang Guang, Kakakin Hukumar Harkokin Hong Kong da Macao, ya fada wa manema labarai yayin wani taron tattaunawa a Beijing cewa “Lokaci dan kalilan ya rage, kafin shugabannin masu zanga-zangar su fuskanci hukunci.”
Makonni da dama da aka yi ana gudanar da zanga-zanga a kan tituna, sun jefa cibiyar hada-hadar kudade ta Asiya cikin mummunan rikicin siyasa, wanda ba a ga irinsa ba tun lokacin da Birtaniya ta mika mulkin yankin ga kasar China a 1997.
Zanga-zangar an fara ta ce a watan Yuni bayan mazauna garin Hong Kong suka fusata da kudirin dokar mika masu aikata laifuffuka ga China don su fuskanci hukunci.
A sanadin wannan tashin hankali aka dakatar da dokar, amma zanga-zangar ta ci gaba kuma tuni ta juye zuwa kira ga neman a canja fasalin mulkin yankin.