✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hatsarin mota ya salwantar da rayukan fiye da mutum 20 a Osun

Mutum fiye da ashirin sun riga mu gidan gaskiya a hatsarin.

Wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan babbar hanyar Ilesa zuwa Akure, ya salwantar da rayukan fiye da mutum 20 a ranar Litinin.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Osun, SP Yemisa Opalolo da ta Hukumar Kiyaye Hadurra (FRSC), Agness Ogunbgemi, sun tabbatar wa da Aminiya lamarin.

Tuni dai jami’an ‘yan sanda da na Hukumar FRSC sun kai dauki inda suka yi gaggawar garzaya wa da wadanda suka jikkata zuwa Asibitin RTC da ke Ipetu-Ijesa tare da killace mutanen da suka mutu a Asibitin Wesley da ke Ilesa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan ta ce hatsarin ya auku ne sakamakon wata babbar motar dankon makamashin gas da ta kwace daga karkashin gudanawarwar matukinta a yankin Igbelajewa na jihar Osun, inda takwararta ta Hukumar FRSC ta ce ba a iya tantance adadin mutanen da hatsarin ya rutsa da su ba.

Mashaida wannan mugun gani sun tabbatar da cewa mutum fiye da ashirin sun riga mu gidan gaskiya a hatsarin ciki har da wadanda suka kone kurmus ta yadda ba a iya gano ko su waye.