✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Akalla mutum 11 suka mutu a sabuwar zanga-zanga a Sudan

Wani rahoto daga kasar Sudan ya bayyana cewa kimanin mutum 11 ne suka mutu a wata zanga-zangar neman maida kasar a kan tafarkin mulkin farar…

Wani rahoto daga kasar Sudan ya bayyana cewa kimanin mutum 11 ne suka mutu a wata zanga-zangar neman maida kasar a kan tafarkin mulkin farar hula.

’Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa a kan dubban masu zanga-zang a ranar Lahadin da ta gabata a Birnin Khartoum, da wasu sassan  kasar.

Da take tofa albarkacin bakinta game da kisan da aka yi ga masu zanga-zangar, Gwamnatin Amurka ta yi Allah wadai da irin karfin da aka nuna a kan masu zanga-zangar.

A halin yanzu kuma, yayin da masu zanga-zangar ke ci gaba da matsa lamba a kan sojojin da suka tumbuke tsohon Shugaban Kasar Sudan Omar al-Bashir,  su hanzarta maida kasar a kan tafarkin dimokuradiyya, akwai alamar cewa kungiyoyin kishin Musulunci suna fuskantar kalubale wajen samun bakin magana a kan makomar kasar kamar yadda Muryar Amurka ta ruwaito.

Wadannan kungiyoyin na ’yan kishin Musulunci sun taka muhimmiyar rawa wajen taimaka wa al-Bashir ya dare kan karagar mulki.

Wannan ya sa ake ganin halin da aka shiga yanzu a Sudan ba zai taimake su samun shiga a cikin kungiyoyin da ke sahun gaba wajen shata sabuwar makomar kasar ba.