Kungiyar likitocin Najeriya ta mayar da martani game da kalaman Ministan Kwadagon Najeriya Chris Ngige, na cewa Najeriya na da wadatattun likitoci don haka kungiyar ta ce, Ministan bai damu da yadda likitcin kasar ke fita zuwa kasashen waje.
Kungiyar likitocin da kwararru a fannin kiwon lafiya sun bayyana cewa, kuncin rayuwa da likitocin ke fama da shi ke sasu fita zuwa wasu kasashen.
Ministan ya bayyana hakan ne a shirin `Sunrise Daily` da talabijin Channels TV ke shiryawa.