Fitaccen jarumin Kannywood, Ali Nuhu ya yi murnar cika shekara 16 da auren matarsa Maimuna.
Ali Nuhu ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa, “Alhamdulillah! Yau mun cika shekara 16. Muna godiya ga Allah SWT da Ya nuna mana wannan ranar, sannan Ya kara dankon soyayya tsakaninmu. ’Yan uwa da abokan arziki a taya mu da addu’a.”