Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya amince tare da tabbatar da mukaddashin Sufeto Janar na ‘yan Sandan Najeriya Muhammad Adamu a matsayin sabon Sufeto Janar na ‘Yan Sanda a yau Alhamis.
Gwamnan jihar Ekiti Dakta Kayode Fayemi, ne bayyanawa wakilinmu hakan bayan taron da suka yi a fadar shugaban kasar a Abuja.
A ranar 15 ga watan Janairu aka baiwa Muhammad Adamu mukamin mukaddashin Sufeto Janar na ‘yan Sandan Najeriya.