A ranar Litinin da ta gabata Hukumar Kwallon Kafa ta Nahiyar Turai (UEFA) ta fitar da Jadawalin Gasar Zakarun Turai (Champions League) zagaye na biyu.
An kasafta yadda kowace kungiya za ta hadu da takwararta a wasannin zagaye na biyu. Za a fara wasannin ne daga ranakun 12 da 13 ga watan Fabrairun badi.