Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya rattaba hannu akan kudirin dokar kirkiro da sabbin masarautu hudu a jihar da suka hada da: Gaya, Rano, Karaye da Bichi wanda duk kansu lardi ne da ke da hakimai karkashin masaratar Kano.
Bayan rattaba hannu a game da amincewar ‘yan majalisar Kano, Gwamnan Kano ya ce, nan bada bata lokaci ba, za a zabi sarakunan a masarautun.