A farkon wannan makon ne aka yi jana’izar mahaifiyar tsohon gwamnan Jihar Legas, Alhaji Bola Ahmed Tinubu, wato Hajiya Habibat Magaji.
Tun daga lokacin ne ake ta tururuwa zuwa gidan tsohon gwamnan domin yi masa ta’aziyya. daya daga cikin mutanen da suka je wa tsohon gwamnan ta’aziyya shi ne tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, wanda ya taya Alhaji Bola Ahmed jimamin rashin da ya yi, wanda ya ce ba na iyalan tsohon gwamnan ba ne ko Jihar Legas kawai, na Najeriya gaba daya.
Tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce marigayiyar ta yi fice wajen agaza wa mai karamin karfi haka kuma ta shahara wajen inganta rayuwar mata da ma ’yan kasuwa, musammam ma masu karamin karfi don haka ta bar gurbin da zai dauki lokaci mai tsawo kafin a samu wanda zai maye shi.
Alhaji Atiku ya sa an yi wa marigayiyar addu’a da fatan Allah Ya kara wa tsohon gwamnan juriyar wannan rashin.
Shi ma tsohon gwamnan da yake wa bakon nasa bayanin yadda marigayiyar ta rasu, ya ce ba shakka ta wuce ta bar shi da kewa kwarai da gaske.
Ya ce hankalinsa kan kara tashi ne duk lokacin da ya shiga dakinta ya ga hotunanta da mutane iri daban-daban, daga masu hannu-da-shuni zuwa masu karamin karfi.
Ita dai Hajiya Habibatu Magaji ta rasu tana da shekaru 96 ne kuma daruruwan jama’a ne suka yi dafifi wajen yi mata rakiya, kana an rufe kasuwanni a duk fadin jihar domin yi mata addu’ar kwanaki 3 da rasuwa.
Rashin Hajiya Habibatu Magaji na Najeriya ne gaba daya Inji Atiku Abubakar
A farkon wannan makon ne aka yi jana’izar mahaifiyar tsohon gwamnan Jihar Legas, Alhaji Bola Ahmed Tinubu, wato Hajiya Habibat Magaji. Tun daga lokacin ne…