Kwamitin gudanarwa na jam’iyyyar adawa ta PDP ta ce, bayan ta kammala tattaunawa da masu fada aji na jam’iyyar sun amince da goyon bayan Sanata Ali Ndume a matsayin shugaban majalisar Dattawan Najeriya tare da Umar Mohammed Bago a matsayin Kakakin majalsar Wakilan Najeriya, wanda ake saran rantsar da su a yau Talata.
Sakataren jam’iyyar PDP na kasa Sanata Umar Ibrahim Tsauri, ne ya sanar da hakan a yau Talata, inda ya ce sun amince da wannan goyon bayan ne sakamakon ganawar da suka yi da jigogin jam’iyyar.