✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Yan bindiga sun kashe dan jigon PDP a Benuwe

Wasu ‘yan bindiga sun kashe dan jigon jam’iyyar PDP Yandev Amaabai, daya daga cikin tsohon shugabannin  jam’iyyar a karamar hukumar Gboko a jihar Benuwe. ‘Yan…

Wasu ‘yan bindiga sun kashe dan jigon jam’iyyar PDP Yandev Amaabai, daya daga cikin tsohon shugabannin  jam’iyyar a karamar hukumar Gboko a jihar Benuwe.

‘Yan bindigar sun kashe yaron mai suna Orkuma Yandev Amaabai, ne a lokacin da yake hanyarsa ta komawa gida ranar Asabar da daddare inda `yan bindigan suka harbe shi.

Kakakin hukumar ‘yan sandan jihar Catherine Anene ya tabattar da aukuwar lamari. A yanzu haka hukumar ‘yan sandan na ci gaba da binciken kisan.